DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya amince da kashe Naira biliyan 712.3 don gyaran filin jirgin saman Lagos

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da ware Naira biliyan 712.3 domin gudanar da cikakken gyaran filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Lagos, a wani bangare na kokarin farfado da bangaren sufurin jiragen sama a karkashin shirin Renewed Hope Infrastructure Development Fund.

Ministan sufurin jiragen sama Festus Keyamo, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Fadar Shugaban Kasa jim kadan bayan taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a Abuja ranar Alhamis.

Keyamo ya bayyana cewa wannan ne karo na farko da za a gudanar da cikakken gyaran tsohon ginin filin jirgin tun daga lokacin da aka gina sa.

A cewarsa, za a kammala aikin cikin watanni 24, kuma yana daga cikin shirin sabunta muhimman ababen more rayuwa da suka hada da sabunta filin saukar jirage da fitilun sauka a Port Harcourt da za a kashe Naira biliyan 42.1bn, da jiha Kano da za a kashe Naira biliyan 46.3bn, sai Lagos da aka ware Naira biliyan 44.1bn, domin rage jinkirin saukar jirage da ke faruwa sakamakon yanayi mara kyau.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara