Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince da ware Naira biliyan 712.3 domin gudanar da cikakken gyaran filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Lagos, a wani bangare na kokarin farfado da bangaren sufurin jiragen sama a karkashin shirin Renewed Hope Infrastructure Development Fund.
Ministan sufurin jiragen sama Festus Keyamo, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Fadar Shugaban Kasa jim kadan bayan taron Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) a Abuja ranar Alhamis.
Keyamo ya bayyana cewa wannan ne karo na farko da za a gudanar da cikakken gyaran tsohon ginin filin jirgin tun daga lokacin da aka gina sa.
A cewarsa, za a kammala aikin cikin watanni 24, kuma yana daga cikin shirin sabunta muhimman ababen more rayuwa da suka hada da sabunta filin saukar jirage da fitilun sauka a Port Harcourt da za a kashe Naira biliyan 42.1bn, da jiha Kano da za a kashe Naira biliyan 46.3bn, sai Lagos da aka ware Naira biliyan 44.1bn, domin rage jinkirin saukar jirage da ke faruwa sakamakon yanayi mara kyau.



