DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ma’aikatan lafiya da ungozomomi a Nijeriya sun janye yajin aikin da suka shiga – In ji Ministan Lafiya

-

Kungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma ta Nijeriya ta janye yajin aikin da ta fara, kamar yadda ministan lafiya, Farfesa Ali Pate ya tabbatar a yau Juma’a bayan wani taron sirri da shugabannin kungiyar.

Ministan ya bayyana wa manema labarai cewa an cimma matsaya tsakanin gwamnati da shugabannin kungiyar, wanda hakan ne ya sa aka dakatar da yajin aikin.

Sai dai shugabannin kungiyar ta ki yin wani bayani ga manema labarai bayan kammala taron.

Tun ranar 29 ga watan Yuli, 2025 ne kungiyar NANNM ta fara yajin aikin gargadi na mako guda saboda kin daukar mataki daga gwamnatin tarayya, bayan kungiyar ta mika wa gwamnati gargaɗi na kwanaki 15 tun daga 14 ga Yuli, 2025.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisun tarayya sun nemi a fallasa masu daukar nauyin ta’addanci a Nijeriya

Majalisun tarayyar Nijeriya sun bukaci gwamnatin ƙasar ta bayyana sunayen mutanen da ke daukar nauyin ta’addanci tare da gurfanar da su a gaban kotu.   Wannan kira...

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Mafi Shahara