Wata sabuwa ta kunno kai a jihar Neja bayan da Gwamna Mohammed Umaru Bago ya bayar da umarnin rufe gidan rediyo na Badeggi FM da ke Minna, babban birnin jihar, lamarin da ya janyo cece-kuce da suka daga kungiyoyin ‘yan jarida da masu kare hakkin ‘yan kasa ciki har da Amnesty International.
A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Bologi Ibrahim ya fitar, gwamna Bago ya bayar da umarnin a rufe gidan rediyon tare da kwace lasisin aikinsa da kuma binciko bayanan mamallakinsa, a yayin wani taron jam’iyyar APC da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar.
Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya zargi gidan rediyon da tayar da fitina da tunzura jama’a kan gwamnati, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Shugaban gidan radiyon na Badeggi FM Abubakar Shuaib, ya mayar da martani ga wannan mataki, yana mai cewa ya kamata gwamnan ya bi hanyar doka wajen gabatar da korafe-korafensa, maimakon tura jami’an tsaro su tsoratar da ma’aikatan rediyon ko mamallakinsa.


