DCL Hausa Radio
Kaitsaye

A wa’adin shekara 4 kawai zan gyara Nijeriya – Peter Obi

-

Tsohon dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi, ya ce idan Allah ya ba shi nasara a zaben 2027, zai yi mulki na wa’adin shekara hudu kacal. Obi ya bayyana hakan ne domin nuna cewa dogon zama a mulki ba shi ne ma’aunin nasara ba.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a jiya, Obi ya yi nuni da manyan shugabanni na duniya kamar Abraham Lincoln, John F. Kennedy da Nelson Mandela, a gajeren lokaci da suka yi a mulki, sun bar tarihi da ci gaba mai ɗorewa.

Obi ya ce manufarsa ita ce shugabanci na gaskiya, cancanta da kafa kyakkyawan tarihi, ba wai yin shekaru da dama a ofis ba.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara