DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Daga cikin rarar tallafin man fetur za a yi wa filin jirgin saman Lagos gyaran Naira biliyan 712 – Festus Keyamo

-

Ministan sufurin jiragen sama na Nijeriya Festus Keyamo, ya kare shirin gwamnatin tarayya na sake fasalta filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Lagos da kudin na suka kai Naira biliyan 712, yana mai cewa hakan na da nufin yin gogayya da sauran filayen na duniya.

Yayin wata hira da tashar Channels Television a shirin Sunday Politics, Keyamo, wanda lauya ne mai matsayin SAN, ya bayyana cewa filin jirgin da aka gina sama da shekaru arba’in da suka wuce ya lalace matuka.

“Rufin tashar jirgin na yayyafa ruwa; wajen ya lalace kuma yana wari. Ana siyar da Indomie da wasu kayayyaki a ciki. Fankoki da ke tura kaya sun daina aiki saboda babu gyara,” in ji shi.

A makon da ya gabata, gwamnatin tarayya ta amince da kashe biliyan ₦712 don yin aikin, wanda hakan ya jawo cece-kuce daga jama’a da dama.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara