DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba kwadayin mulki ne ke saka Peter Obi yawan takara ba a Nijeriya – Chimamanda Adichie

-

Fitacciyar marubuciyar nan, Chimamanda Ngozi Adichie, ta bayyana cewa goyon bayanta ga dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, yana da nasaba da yadda ta ke ganin jajircewarsa da kishinsa ga ci gaban Najeriya.

A wata hira ta musamman da aka yi da ita a da gidan talabijin na Channels, Adichie ta ce Obi ya bambanta da yawancin ‘yan siyasa, domin ba girman kai ko kwadayin mulki ke tura shi yin takara ba.

Google search engine

Akwai mutane da dama da ke neman mulki saboda girman kai, ba don suna da wata niyyar gyara kasar ba” in ji Chimamanda.

Chimamanda ta kara da cewa dabi’un Obi na kaskantar da kai, gaskiya da rikon amana, suna daga cikin abubuwan da suka bambanta shi da sauran ‘yan takara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara