DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Lamido ya nemi a kori su Wike, Ortom, Ikpeazu da duk ‘yan PDPin da suka yi wa APC kamfe a 2023

-

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bukaci a kori ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, da tsohon gwamnan Benue, Samuel Ortom, da tsohon gwamnan Abia, Okezie Ikpeazu, da sauran ‘yan jam’iyyar PDP da suka yi wa APC kamfen a zaɓen 2023.

Lamido, ya yi wannan magana ne a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, inda ya ce lokaci ya yi da shugabancin PDP zai ɗauki matakin ladabtarwa kan ‘yan jam’iyyar da ke cin amanar jam’iyya, yana mai zargin su da shirye-shiryen sake goyon bayan APC a 2027.

Google search engine

Ya kuma nuna damuwa kan yadda rashin ladabtar ‘yan jam’iyya ke ci gaba da zama al’ada tun bayan taron fidda gwani na 2022.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in...

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025...

Mafi Shahara