DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Indiya na siyan danyen man Najeriya, yayin da matatar Dangote ke shigo da nata daga Amurka

-

Rahoton jaridar Punch ya tattaro cewa matatar mai ta Dangote da ke Legas tana samun yawancin danyen man da take sarrafawa daga Amurka, yayin da matatun mai na Indiya ke siyan mai daga Najeriya.

Rahotanni sun nuna cewa kamfanin Indian Oil ya sayi ganga miliyan daya ta danyen man Agbami daga Najeriya wanda zai isa a watan Satumba, yayin da BPCL ta kuma kulla yarjejeniyar siyan ganga miliyan biyu na man Najeriya har zuwa watan Satumba da Oktoba.

Google search engine

Sai dai, kididdigar Kpler ta nuna cewa a watan Yuli, kaso 60 cikin 100 na man da matatar Dangote ta shigo dashi daga Amurka ne da kiyasin gangar dubu 370 a rana, yayin da kaso 40 cikin 100 ya zama daga Najeriya.

A baya dai, Dangote ya bayyana cewa matsalar samun wadataccen danyen mai daga cikin gida na daga cikin dalilan da suka sa yake dogaro da shigo da na waje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara