DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Trump ya bukaci a gaggauta korar marasa matsuguni wato homeless daga babban birnin Amurka Washington

-

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya umarci a gaggauta korar marasa matsuguni daga birnin Washington DC, yana mai cewa za a samar musu da wuraren zama amma nesa da babban birnin.

A wani saƙo da ya wallafa a Truth Social tare da hotunan tantuna da tarkacen da ke gefen titi, Trump ya ce masu aikata laifi za a tura su gidan yari.

Google search engine

Rahoton gidan talabijin na Channels ya ambato shi na bayyana cewa birnin zai zama mafi tsaro da tsabta fiye da da, kuma ya soki magajin garin birnin, Muriel Bowser.

Rahotanni sun nuna cewa gwamnatin tarayya na shirin tura sojojin National Guard don aiwatar da wannan umarni, duk da cewa ba a yanke hukunci na ƙarshe ba.

Kwanaki biyu da suka gabata, Trump ya bayyana cewa zai dauki mataki kan marasa matsuguni da ke kusa da Fadar White House.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara