DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An yi sabon sulhu da ‘yan bindiga a Safana jihar Katsina

-

Rahoton jaridar Daily Trust ya ce karamar hukumar Safana a jihar Katsina ta shiga yarjejeniyar sulhu da ‘yan bindiga, kamar yadda Jibia, Batsari, da Danmusa suka riga suka yi, domin kawo karshen hare-hare a yankin.

Taron sulhun ya gudana a bakin dajin Gimi, Runka, karkashin jagorancin shugaban karamar hukumar, Abdullahi Sani Safana, tare da Yariman Katsina, Alhaji Sada Rufa’i, da sauran shugabannin gargajiya.

Google search engine

Bangarorin biyu sun amince da janye rikici da gaba a tsakani, tare da bada damar yin noma da walwala ba tare da tsangwamar kowa ba.

Sharuɗɗan yarjejeniyar sun haɗa da dakatar da hare-hare, daukar rayuka, da sace mutane, da kuma bai wa makiyaya damar zuwa kasuwa, asibiti, da sauran wuraren hidima ba tare da cin zarafi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara