Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya amince da nadin Farfesa Yakubu Yunusa Musa a matsayin sabon shugaban hukumar Alhazai ta jihar, inda zai maye gurbin Alhaji Mohammed Dawule Mainok.
Wata sanarwa daga mai bai wa gwamna shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Dauda Iliya, ta bayyana cewa Farfesa Musa, ɗan asalin karamar hukumar Shani, ya kasance gogaggen malami kuma mai kwarewa a shugabanci.
Kafin wannan mukami, Farfesa Musa ya jagoranci Cibiyar kasa da kasa ta kimiyyar Alkur’ani a jami’ar Khalifa Isyaku Rabiu da ke Kano, sannan kuma Farfesa a fannin karatun Larabci.
Haka zalika, sanarwar ta ce ya kasance mamba a hukumar ilimin Larabci da tsangaya ta jihar Borno, tare da rike manyan mukaman ilimi da na gudanarwa a ciki da wajen jami’o’i.




bawabasainai@gmail.co