Sojojin Najeriya sun yi nasararr kawo karshen wasu masu tayar da kayar baya da dama a kareto, da ke karamar hukumar Mobbar, jihar Borno, bayan yunƙurin kwanton-bauna da ya ci tura.
Ababen fashewa da ‘yan ta’addan suka dasa sun tarwatsa su, inda biyar suka sheka barzahu nan take.
Rahoton gidan talabijin na Channels ya ce an kwato makamai iri-iri da gadan albarusai da kuma harsasai masu yawa, gami da wasu ababen fashewa guda biyu da wasu kayayyaki.



