DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP na barazanar hukunta Wike kan babban taron da za ta yi a watan Nuwamba

-

Jam’iyyar PDP ta yi gargadi cewa ba za ta yi jinkiri wajen hukunta duk wani mamba da ya saba wa kundin tsarin jam’iyyar ba, biyo bayan kalaman da Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya yi kan babban taron ta na kasa da jam’iyyar ta shirya gudanarwa a watan Nuwamba.

A cikin wata hira da ya yi da manema labarai a ranar Talata, Wike ya ce bai san da wani babban taro da za a yi ba, tare da jaddada cewa shi da abokan tafiyarsa za su kalubalanci duk wani abu da suka ga kamar rashin adalci ne.

Google search engine

Ya kuma yi korafi cewa ba a turo masa sanarwar taron kwamitin NEC ba, yana mai cewa zai kalubalanci tsarin idan bukatar hakan ta taso.

Sai dai mai magana da yawun PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya musanta ikirarin Wike, inda ya bayyana cewa an kira NEC bisa ka’ida, an turo sanarwa, kuma hukumar INEC ma ta samu takardar a hukumance.

Ologunagba ya tabbatar da cewa taron zai gudana a Ibadan, Jihar Oyo, daga ranar 15 zuwa 16 ga watan Nuwamba, 2025, inda ya jaddada cewa shiri na tafiya yadda ya kamata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara