DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hisbah a jihar Kano za ta dauki nauyin aurar da tubabbun ‘yan daba

-

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana shirin ta na ɗaukar nauyin auren wasu matasa da suka ajiye makamai tare da yin alkawarin barin ayyukan daba da tashin hankali.

Kwamandan hukumar Hisbah, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ne ya bayyana haka bayan sama da matasa 1,000 sun ajiye makaman su tare da rungumar zaman lafiya.

Google search engine

Sheikh Daurawa ya ce wannan shiri na daga cikin manufofin Gwamna Abba Kabir Yusuf, wajen ba da damar gyara rayuwa da inganta makomar matasa da ke aikata laifi.

Ya gargade su da su zama mutane na gari tare da kira da sauran da ke irin wannan dabi’a su dawo domin rungumar zaman lafiya.

An gudanar da taron ne a Hedikwatar hukumar ‘yan sandan jihar Kano da ke Bompai,tare da sauran jami’an tsaro da masu ruwa da tsaki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara