Sojojin Nijeriya sun yi nasarar halaka ‘yan bindiga 7, tare da kwato babura a wani samame da suka kai kauyen Baba da ke Karamar Hukumar Kankara ta jihar Katsina.
Kwamishinan tsaron cikin gida na jihar Katsina,Nasir Mu’azu, ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai a ranar Juma’a a Katsina.
Ya ce artabun da aka yi da ‘yan ta’addan ya dauki tsawon sa’o’i biyu a ranar Alhamis, 21 ga watan Agusta, 2024, bayan samun sahihan bayanan sirri kan motsin ‘yan ta’addan da ke addabar al’umman manoma a yankin.
Dakarun sojoji sun yi gaggawar kai farmaki inda suka fatattaki ‘yan bindigar, suka kashe bakwai daga cikinsu, sauran kuma suka tsere da raunukan harbin bindiga, sojojin sun kwato babura hudu da ‘yan ta’addan ke amfani da su wajen aikata miyagun laifuka.
Ya ce wannan nasara na cikin ci gaban ayyukan sojojin da ake gudanarwa a kananan hukumomin da ke fuskantar barazanar tsaro, da nufin lalata mafakar ‘yan ta’adda da tabbatar da zaman lafiya domin inganta harkokin noma a wannan lokacin.



