DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hadakar ADC yaudarar ‘yan Nijeriya take yi – in ji Datti Baba Ahmed

-

Datti Baba-Ahmed, tsohon ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, ya bayyana cewa haɗakar adawa da aka kafa a ƙarƙashin jam’iyyar ADC ba gaskiya ba ce, kuma tana yaudarar ‘yan Najeriya da ikirarin ceto ƙasar daga halin da take ciki.

Baba-Ahmed ya bayyana haka ne a cikin shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels a ranar Juma’a, inda ya ce: “Suna yaudarar mu,” yana mai jaddada rashin amincewarsa da tsarin.

Google search engine

Ya tuna cewa shi ne ya tsaya tare da Peter Obi a matsayin mataimaki a zaben shugaban ƙasa na 2023, wanda tsohon gwamnan Legas, Bola Tinubu na jam’iyyar APC ya lashe zaben.

Sai dai a cikin wannan hirar, Baba-Ahmed ya bayyana cewa ya shirya sake zama ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa tare da Obi a zaben 2027 idan aka samu dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara