DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin sojin Guinea ta dakatar da manyan jam’iyyu uku a kasar

-

Gwamnatin sojin kasar Guinea ta dakatar da manyan jam’iyyun siyasa uku na tsawon watanni uku, ciki har da jam’iyyar tsohon shugaban ƙasa Alpha Condé.

Wannan mataki ya zo ne daidai lokacin da ake shirin gudanar da kuri’ar raba gardama kan sabon kundin tsarin mulki a ranar 21 ga Satumba, karkashin jagorancin Janar Mamadi Doumbouya wanda ya karɓi mulki a juyin mulki a shekarar 2021.

Google search engine

Rahotanni sun ce dakatarwar ta faru ne ’yan kwanaki kafin zanga-zangar da ’yan adawa suka shirya a ranar 5 ga Satumba, domin nuna adawa da mulkin Doumbouya.

Sai dai manyan jam’iyyu da ƙungiyoyin farar hula sun yi watsi da tsarin rubuta sabon kundin mulki, suna masu cewa wata hanya ce kawai ta ƙarfafa mulkin soja a ƙasar, kamar yadda DW Africa ta tabbatar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara