DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin PDP sun gargadi Wike kan yunkurin kawo cikas ga babban taron jam’iyyar

-

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ta yi gargaɗi ga Ministan Abuja, Nyesom Wike, da wasu mambobin jam’iyyar kan yunkurin da zai iya lalata babban taron jam’iyyar da aka shirya gudanarwa a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 ga Nuwamba, 2025.

Hakan na cikin sanarwar bayan taron gwamnonin karo na bakwai da aka gudanar a Gusau, Jihar Zamfara, ranar Asabar, 23 ga Agusta, 2025.

Google search engine

A cewar rahoton gidan talabijin na Channels, gwamnonin sun sake nanata goyon bayansu ga ƙudirin kwamitin zartarwa na ƙasa NEC na PDP karo na 101 da aka gudanar a watan Yuli, wanda ya amince da shirin babban taron jam’iyyar.

Taron na Gusau, ƙarƙashin jagorancin gwamnan Bauchi, Bala Mohammed, ya kuma tattauna kan halin da ƙasar ke ciki, matsalolin tsaro, raguwar darajar dimokuraɗiyya, da shirye-shiryen babban taron PDP mai zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara