DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisar dokokin Nijeriya 53 ne suka yi zaman dumama kujera tsawon shekara daya ba su ba da gudunmuwa a majalisa ba

-

Aƙalla mambobin Majalisar Wakilai 48 da Sanatoci 5 sun kasa shiga wata muhawara, daukar nauyin kudurori ko gabatar da koke-koke a majalisar dokoki cikin tsawon watanni 12, a cewar wani sabon rahoto da aka fitar a ƙarshen mako.

Rahoton ya fito ne daga Deliberative Barometer and Policy-Focus Productivity Report (NASS-DBPFR), wanda Erudite Growth and Advancement Foundation (ERGAF-Africa) ta wallafa, inda aka bibiyi ayyukan majalisa daga ranar 14 ga Yuni, 2023 zuwa 13 ga Yuni, 2024.

Google search engine

A cewar rahoton, waɗannan ‘yan majalisar ba su yi ko da ɗaya daga cikin ayyukan zaman majalisa ba a lokacin da aka duba. An jaddada cewa gazawarsu na shiga muhawarar majalisa ko daukar nauyin kudurori na rage ingancin doka da kuma saɓa tsarin mulkin dimokuraɗiyya.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara