DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar ASUU a Nijeriya ta yi barazanar koma wa yajin aiki

-

Kungiyar malaman jami’o’i a Najeriya ASUU ta yi gargadin cewa za ta iya shiga yajin aikin gama gari, sakamakon gazawar gwamnatin tarayya wajen cika bukatunta.

Jaridar Punch ta ruwaito shugaban ASUU na jami’ar Akure, Farfesa Adeola Egbedokun ya na cewa har yanzu gwamnati ba ta aiwatar da yarjejeniyar 2009 ba, ba ta inganta ɗaukar nauyin jami’o’i ba, sannan akwai bashin albashi da matsalolin daga matsayin malamai da ake ta jinkirta wa.

Google search engine

Ya ce, lokaci ya kure, hakurin ASUU ya kai ƙololuwa, don haka ya roƙi majalisar dokoki, shugabannin addini da na gargajiya, tare da ɗalibai, su shigo lamarin dan gwamnati ta yi abinda ya dace.

Egbedokun ya yi gargadin cewa idan gwamnatin Tinubu ta kasa ɗaukar mataki bayan taron da aka shirya ranar 28 ga watan Agusta, to ASUU za ta ɗauki mataki mai tsauri wanda zai iya shafar makomar jami’o’in Gwamnati a fadin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara