DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta umurci bankuna 6 su bayar da bayanai kan asusan Omoyele Sowore

-

Wata Babbar kotun tarayya da ke Abuja a Najeriya, ta umurci bankuna guda shida su mika wa Sufeto Janar na ‘yan sanda bayanan asusun Omoyele Sowore tun daga watan Janairu 2024 zuwa yanzu.

Mai shari’a Emeka Nwite ne ya bayar da wannan umarni bayan mika bukatar neman izinin yin hakan da lauyan IGP Wisdom Madaki ya yi.

Google search engine

Jaridar Daily Nigerian ta ce ’yan sanda na zargin Sowore, wanda shi ne mai kafar Sahara Reporters da hannu a harkokin ɗaukar nauyin ta’addanci, wanke kuɗi da kuma wasu ayyukan zamba.

Bankunan da abin ya shafa sun haɗa da: UBA, GTBank, Zenith Bank, Opay, Moniepoint da Kuda Microfinance Bank.

Kamfanin dillancin labaran Nijeriya ya nuna cewa sama da asusun banki 26 da ake dangantawa da Sowore ne kotu ta bayar da umarni a bincika domin taimaka wa jami’an tsaro wajen gudanar da nasu bincike.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara