DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta umurci bankuna 6 su bayar da bayanai kan asusan Omoyele Sowore

-

Wata Babbar kotun tarayya da ke Abuja a Najeriya, ta umurci bankuna guda shida su mika wa Sufeto Janar na ‘yan sanda bayanan asusun Omoyele Sowore tun daga watan Janairu 2024 zuwa yanzu.

Mai shari’a Emeka Nwite ne ya bayar da wannan umarni bayan mika bukatar neman izinin yin hakan da lauyan IGP Wisdom Madaki ya yi.

Google search engine

Jaridar Daily Nigerian ta ce ’yan sanda na zargin Sowore, wanda shi ne mai kafar Sahara Reporters da hannu a harkokin ɗaukar nauyin ta’addanci, wanke kuɗi da kuma wasu ayyukan zamba.

Bankunan da abin ya shafa sun haɗa da: UBA, GTBank, Zenith Bank, Opay, Moniepoint da Kuda Microfinance Bank.

Kamfanin dillancin labaran Nijeriya ya nuna cewa sama da asusun banki 26 da ake dangantawa da Sowore ne kotu ta bayar da umarni a bincika domin taimaka wa jami’an tsaro wajen gudanar da nasu bincike.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Akwai bukatar Akpabio da Abbas su yi bayanin yadda aka kashe fiye da naira biliyan 18 a ginin ofishin hukumar majalisar dokokin Nijeriya –...

Kungiyar kare haƙƙin jama’a da tabbatar da shugabanci na gaskiya a Nijeriya SERAP ta nemi shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen...

Abin takaici ne ganin yadda Nijeriya ke cikin kasashen da talauci ya yi wa lahani – Atiku Abubakar

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana talauci a matsayin mafi girman maƙiyi da ɗan Adam ya taɓa sani. A cikin wata sanarwa da ya...

Mafi Shahara