DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun dauki alhakin faduwar jirgin fasinjan Kaduna zuwa Abuja – Hukumar NRC

-

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Nijeriya (NRC), Kayode Opeifa, ya bayyana cewa ya ɗauki cikakken alhakin hatsarin da ya rutsa da jirgin fasinjan Abuja zuwa Kaduna a ranar Talata.

Shugaban ya ce hatsarin bai yi sanadiyyar mutuwar wani ba, abin da ya kira “rufin asirin Allah” domin irin wannan haɗari kan munana a wasu lokutan.

Google search engine

Duk da haka, ya tabbatar da cewa mutane huɗu daga cikin fasinjoji sun samu mummunan rauni, yayin da wasu biyu aka sallame su daga asibiti nan take.

Opeifa ya bayyana cewa hatsarin bai kamata ya faru ba, kuma NRC za ta tabbatar da cewa irin haka ba zai sake faruwa ba.

A yayin tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, ya ce Yanzu haka sun dakatar da hanyar Warri-Itakpe makonni uku da suka gabata saboda tsaro, inda ake yin gyaran manyan layin jirgin domin gujewa irin wannan matsala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara