DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba zan yi takara da Shugaba Tinubu Tinubu a 2027 ba – Wike

-

Ministan birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya bayyana cewa ba zai tsaya takarar shugabancin ƙasa a shekarar 2027 ba.

Wike, wanda tsohon Gwamnan Jihar Rivers ne, ya bayyana haka ne a ranar Litinin yayin wata ganawa da manema labarai a Abuja.

Google search engine

Ya ce duk da cewa jam’iyyar PDP ta kebe tikitin takarar shugabancin ƙasa ga yankin Kudu, bai dace ya tsaya takara ba a lokacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda ya naɗa shi a mukamin Minista.

Wike ya ƙara da cewa wannan matsaya tasa ba ta da alaƙa da neman dama a siyasa, sai dai ya yi haka ne domin biyayya da kuma ka’ida.

Haka zalika, tsohon gwamnan ya bayyana cewa da ba don ƙaunar da yake yi wa jam’iyyar PDP ba, da tuni ta shuɗe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara