DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matsalar tsaro ta ragu a karkashin mulkin Tinubu a Arewa ta tsakiyar Nijeriya – APC Forum

-

Ƙungiyar APC North-Central Forum ta zargi tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, da yaɗa ƙarya da farfaganda kan tsaron Arewa ta tsakiyar Nijeriya.

El-Rufai ya yi zargin cewa matsalar tsaro ta ƙara ta’azzara a yankin karkashin mulkin Shugaba Bola Tinubu, tare da ikirarin cewa gwamnatin tana biyan kuɗi ga ’yan ta’adda.

Google search engine

Sai dai a martanin da ta fitar a ranar Litinin, ƙungiyar APC Forum ƙarƙashin jagorancin Alhaji Saleh Zazzaga ta ce sabanin zargin El-Rufai, gwamnatin Tinubu ta rage matsalar tsaro a yankin tun bayan da ta karɓi mulki a 2023.

Ya ce matsalar tsaro yanzu ta ragu idan aka kwatanta da lokacin baya, a da manoma ba sa iya zuwa gona saboda tsoron hare-hare, amma yanzu suna iya zuwa gonakinsu saboda umarnin da Shugaba Tinubu ya bai wa jami’an tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara