DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wadanda idanunsu suka rufe wajen son mulki ne kawai ke cewa a tunbuke Shugaba Tinubu daga mulkin Nijeriya – Onanuga

-

Mai bai wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu shawara kan harkokin yada labarai da dabarun siyasa, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa masu kira da a sauke shugaban kasa daga mulki ba komai ba ne face ‘yan siyasa masu kwaɗayin mulki.

Onanuga ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin, inda ya mayar da martani kan hirar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi a tashar Channels Television a daren Lahadi.

Google search engine

Ya zargi El-Rufai da kasancewa a sahun gaba wajen neman sauke shugaban kasa, duk da cewa shi kansa ya taba bayyana cewa shekara hudu ba ta isa wani shugaba ya kawo gagarumin sauyi ba.

Onanuga ya yi ikirarin cewa gwamnatin Tinubu ta samu nasarori a cikin shekaru biyun da ta yi, ciki har da ƙaruwa kuɗaɗen shiga ga kasa da sauran abubuwan ci gaba.

1 COMMENT

  1. Gaskiya Onanuga qarya kake, mu Talakawa zamu fada maka Halin qunci da muka shiga sakamakon Manufofin Gwamnatinku marasa amfani. Amma Insha’allahu daga 2027 TINUBU ya gama cin TALIYAR Qashe a VILA, ka rubuta ka aje

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara