Shugaban kasar Ghana, John Mahama, ya tsige babbar Alkaliyar kasar Gertrude Torkornoo, daga mukaminta na babbar Alkaliyar kasar.
Wannan mataki ya biyo bayan rahoton wani kwamiti da aka kafa domin bincikar ta a kan ayyukan da take yi, inda rahoton ya bayar da shawarar a sauke ta daga mukamin.
Torkornoo ta zama shugabar alkalan Ghana ta farko a ‘yan shekarun nan da aka tsige daga mukami karkashin tanadin kundin tsarin mulki ƙasar.



