DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fa’iza Abdulkadir, mai aikin shara da goge-goge da ta mayar da Naira miliyan 4.8 ta samu kyautar miliyan 2.5

-

Matar da ke aikin shara da goge-goge a asibitin koyarwa na jami’ar Maiduguri Faiza Abdulkadir, wadda ta mayar da naira miliyan 4.8 da aka tura mata a asusun bankinta bisa kuskure, ta samu kyautar naira miliyan 2.5 daga wani mutum da ba a bayyana sunansa ba.

An mika mata wannan tallafi ne a ranar Litinin a Maiduguri ta hannun shugabar ƙungiyar Da’awah Wal Irshaad Women Organisation ta jihar Borno, Hajiya Aisha Muhammad Aisami, wadda ta ce mutumin ya karanta labarin matar ne a jaridar Daily Trust sannan ya bukaci a nemo ta domin a karfafa mata gwiwa.

Google search engine

A matsayin ta na ma’aikaciyar asibitin, Fa’iza na samun albashin N30,000 kacal a kowane wata, tana kuma daukar nauyin mahaifiyarta da kuma ‘ya’yanta guda biyar.

Tun da fari matar gwamnan jihar Borno, Dr Falmata Babagana Zulum, ta yi mata kyautar Naira miliyan guda tare da kayan abinci da kayan koyon sana’o’in dogaro da kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara