DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Legas ce cibiyar kasuwancin Nijeriya – Martanin Daniel Bwala ga masu sukar manyan ayyukan gwamnatin tarayya a jihar

-

Mai bai wa shugaban Najeriya Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai Daniel Bwala, ya ce jihar Legas ta kowa ce, sannan ta kasance alfaharin tattalin arziƙin kasar.

A cikin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise ranar Laraba, Bwala ya ce mayar da hankalin gwamnatin tarayya wajen aiwatar da manyan ayyuka a Legas ba son kai ba ne, illa dai saka jari ne a cibiyar kasuwancin ƙasar.

Google search engine

A cewarsa attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka Dangote dan Arewa ne, amma kasuwancinsa yana Legas, kuma dukkan manyan masu kudi a Najeriya suna da jari a jihar.

Bwala ya kwatanta Legas da biranen kasuwanci na duniya irin su London, New York da Paris, inda ya ce cibiyar tattalin arziƙin ƙasa na samun mafi yawan ayyukan gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara