Mai bai wa shugaban Najeriya Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai Daniel Bwala, ya ce jihar Legas ta kowa ce, sannan ta kasance alfaharin tattalin arziƙin kasar.
A cikin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise ranar Laraba, Bwala ya ce mayar da hankalin gwamnatin tarayya wajen aiwatar da manyan ayyuka a Legas ba son kai ba ne, illa dai saka jari ne a cibiyar kasuwancin ƙasar.
A cewarsa attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka Dangote dan Arewa ne, amma kasuwancinsa yana Legas, kuma dukkan manyan masu kudi a Najeriya suna da jari a jihar.
Bwala ya kwatanta Legas da biranen kasuwanci na duniya irin su London, New York da Paris, inda ya ce cibiyar tattalin arziƙin ƙasa na samun mafi yawan ayyukan gwamnati.



