DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kimar Nijeriya ta dawo a idon duniya cikin mulkin Shugaba Tinubu na tsawon shekaru biyu, in ji fadar shugaban kasa

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce manufofin tattalin arziƙin gwamnatinsa sun fara haifar da sakamako mai kyau, inda tattalin arziƙin ƙasar ya fara daidaita tare da jawo mata kima a idon duniya.

Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Talata lokacin da ya karɓi bakuncin Sarkin Ogbomosoland, Oba Ghandi Afolabi Oladunni Olaoye, tare da wasu sarakunan gargajiya a fadarsa da ke Abuja.

Google search engine

Ya ce cin hanci da rashawa sun lalata tattalin arziƙin ƙasar, amma yanzu saboda matakan da aka dauka kasar ta fara farfadowa.

Shugaban ya kuma bayyana kafa asusun NELFUND a matsayin matakin tabbatar da cewa babu wani ɗalibi zai daina karatu saboda talauci, yana mai cewa ilimi shi ne makami mafi dacewa wajen yakar talauci.

1 COMMENT

  1. Gaskiya wannan Maganar ta Mr. T-Pain Ƙarya Tsagwaronta, saboda Talakawan Nigeria sun shiga Hali na Ƙuncin da basu taɓa shiga ba. Sakamakon Manufofin marasa amfani ga Talaka

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara