DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Tinubu ba ta amfani da hukumomin yaki da rashawa don farautar ‘yan adawa – Mohammed Idris

-

Ministan yada labaran Najeriya Mohammed Idris, ya musanta zargin cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu na amfani da hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa wajen musgunawa ‘yan adawa.

Wannan martanin nasa na zuwa ne bayan tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin da amfani da hukumar EFCC wajen musgunawa ‘yan adawa a shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027.

Google search engine

Idris ya yi wannan jawabi ne a ranar Laraba yayin buɗe taron tattaunawa da hukumar ICPC ta shirya a Abuja kan rawar da kwamishinonin yaɗa labarai na jihohi za su taka wajen yaƙi da rashawa.

Ya ce gwamnatin Tinubu ba ta tsoma baki domin tabbatar da cewa hukumomin EFCC da ICPC suna gudanar da ayyukansu ba tare da fuskantar matsin lamba daga gwamnati ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara