DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin tabbatar da inshorar lafiya a dukkanin hukumomi da ma’aikatun gwamnatin Nijeriya

-

Shugaba Bola Tinubu ya umarci sakataren gwamnatin tarayya da ya fitar da takardar umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomi domin tabbatar da inshorar lafiya bisa tanadin dokar inshorar lafiya ta shekarar 2022.

Sai dai shugaban kasar ya jaddada bukatar ci gaba da tattaunawa da ɓangarori masu zaman kansu domin tabbatar da cewa dokar ba ta kawo tangarda ga kowane bangare ba.

Google search engine

Ya ce dukkanin ma’aikatu da hukumomi za su sanya ma’aikatansu a tsarin, kuma duk wani kamfani ko kungiya da ke son kulla alaka da gwamnati dole sai ya gabatar da takardar shaida da hukumar inshorar lafiya NHIA ta bayar, yana mai cewa idan babu ita gwamnati ba za ta kulla wata yarjejeniya da wani kamfani ko kungiya ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara