DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sake nada kwamishinoni

-

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da nadin wasu mukamai na wasu muhimman mutane a gwamnatinsa ciki har da Ahmad Muhammad Speaker a matsayin mashawarci kan yada labarai.
Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce sauran mukaman sun hada da Injiya Ahmad a matsayin mai baiwa gwamna shawara bangaren ayyuka da Malam Sani Abdullahi Tofa bangaren ayyuka na musamman.
Gwamnan ya kuma nada Malam Sani Tofa a matsayin Khadi na kotun shari’a, kazalika da da Honarabul Ibrahim Jibrin Fagge a matsayin shugaban hukumar kula da ma’aikatan kananan hukumomi da sai Hajia Ladidi Ibrahim Garko a matsayin shugabar hukumar kula da ma’aikatan jihar Kano.
Sanarwar ta ce, gwamnan zai rantsar da wadanda aka baiwa mukaman a gobe Litinin 6 ga watan Janairun a fadar gwamnatin jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara