DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Lauyan Natasha ya zargi Akpabio da kokarin amfani da kujerarsa wajen daukar fansa kan sanatar

-

Lauyan Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, Victor Giwa, ya zargi shugaban majalisar dattawan Najeriya Godswill Akpabio, da amfani da mukaminsa wajen daukar fansa kan ‘yar majalisar.

Giwa ya bayyana haka ne a cikin wata hira da aka yi da shi a shirin siyasar gidan talabijin na Channels a ranar Talata, inda ya bayyana matakin da majalisar dattawan ta dauka a kan Natasha a matsayin bi-ta-da-kulli.

Google search engine

A cewar lauyan, wa’adin hukuncin dakatar da ita na tsawon watanni shida ya cika, amma duk da haka majalisar ta ki amince mata da komawa bakin aiki.

Ya ce wannan hali da ake nuna wa Natasha ya jefa ayar tambaya kan abubuwan da sanatar ta fada a baya, yana mai cewa ya kamata a bari lokaci da tarihi su nuna gaskiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara