DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Masu kiran a sauya hafsoshin tsaron Nijeriya na da wata boyayyar manufa – Ali Ndume

-

Sanata Ali Ndume mai wakiltar Borno ta Kudu, ya roki Shugaba Bola Tinubu da cewa kar ya saurari kiran a sauke manyan hafsoshin tsaron Nijeriya.

A cewarsa, irin wannan kira zai iya karya gwiwar rundunonin soji a daidai lokacin da ake bukatar hakan wajen yaki da ayyukan ta’addanci.

Google search engine

Kungiyar “Northern Ethnic Nationalities Forum” ce ta yi kira a farkon makon nan da a gaggauta sauke hafsoshin tsaro, tana mai cewa ba su da kwarewar da ake bukata wajen shawo kan matsalar tsaro duk da makudan kudaden da ake ware wa bangaren cikin kasafin kudi.

A bangare guda, Ndume ya ce matsalolin tsaron Nijeriya sun fi danganta ne da rashin isassun kayan aiki da kuma rashin kulawa ga walwala sojoji.

Ya jaddada cewa abin da ake bukata shi ne horo, kayan aiki, da kuma kwarin gwiwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara