DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jonathan da Obi sun gana yayin da tattaunawa kan zaben 2027 ke daukar zafi

-

Tsohon shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan, da dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, sun gana a Abuja a ranar Alhamis.

Ganawar ta zo ne a daidai lokacin da ake ƙara samun tattaunawa kan yiwuwar jam’iyyun adawa su haɗa kai domin fitar da ɗan takara mai ƙarfi a zaben 2027 domin kalubalantar shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Google search engine

A watan Agusta, wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar PDP sun tabbatar da cewa ana ci gaba da ƙoƙarin shawo kan Jonathan ya dawo ya tsaya takarar shugaban ƙasa a matsayin ɗan takarar jam’iyyar.

Jonathan, wanda ya shugabanci Najeriya daga 2010 zuwa 2015, har yanzu yana daga cikin fitattun ‘yan siyasar ƙasar.

Rahoton jaridar Daily Trust ya ayyana Obi, tsohon gwamnan Anambra na tsawon wa’adi biyu, ya samu karɓuwa sosai bayan zaben 2023, inda ya zo na uku amma ya kayar da Tinubu a jihar Legas, inda shi ne gari da aka fi sanin shugaban ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara