DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nan kusa ‘yan Nijeriya za su fara samun hasken wutar lantarki babu daukewa – Adebayo Adelabu

-

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta ce an kusa cimma burin samar da wutar lantarki babu daukewa a fadin kasar.

Ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu ne ya bayyana haka a Abuja yayin kaddamar da gine-gine da dakuna a cibiyar horar da ma’aikatan wutar lantarki ta kasa NAPTIN.

Google search engine

Adelabu ya ce wannan ci gaban ya nuna jajircewar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu wajen fifita bukatun al’umma, inda ya ce yanzu haka an samu mafi karfin wutar da aka taba samarwa a tarihin Nijeriya.

A cewarsa nan kusa za a shiga wani zamani da Nijeriya za ta rika samun wutar lantarki ta tsawon awanni 24 ba tare da yankewa ba.

Ya kuma ce Nijeriya na da dukkan abin da ake bukata wajen fara kera na’urorin wutar lantarki kamar mita, transfoma, da batir wanda zai sa ta dogara da kanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara