DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Farashin kayan abinci ya sauka a fadin Nijeriya – Ministan Noma

-

Ministan Noma a Nijeriya Abubakar Kyari, ya bayyana cewa an samu saukar farashin kayan abinci a fadin Nijeriya.

Ministan ya yi wannan bayani ne a wata tattaunawa da aka yi da shi a gidan talabijin na ARISE ranar Juma’a.

Google search engine

A cewarsa, matakan da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dauka wajen tabbatar da harkokin noma sun fara tasiri, inda ya ce gwamnatin tarayya ta yi amfani da dabaru wajen shigo da wasu kayayyakin abinci domin magance matsalolin da suka dade suna damun harkokin noma a Nijeriya.

Ya bayyana cewa akwai gibin samar da kayayyakin abinci da ake fuskanta, inda ya ce a shinkafar da ake nomawa a kasar, akwai gibin kashi 15% tsakanin abin da ake bukata da kuma abin da ake samarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara