DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ƴan majalisar tarayya daga jihar Kebbi sun bukaci jami’an tsaro su kama Malami

-

Wani rikicin siyasa ya kunno kai a jihar Kebbi bayan ‘yan majalisar tarayya daga jihar suka fito fili suna zargin tsohon Ministan Shari’a kuma tsohon Antoni Janar na Tarayya, Abubakar Malami, da yada labarai na karya da suke ganin za su iya jefa jihar da kasa baki daya cikin rudani.

A wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja, jagoran ƴan majalisar, Sanata Adamu Aliero, ya bukaci hukumomin tsaro da su gaggauta kama tare da gurfanar da Malami a gaban kotu bisa zargin kokarin tayar da tarzoma da tada hargitsi a jihar.

Sanata Aliero ya ce Malami ya shigo da ‘yan daba daga Sokoto da wasu makwabtan jihohi domin su kai hari kan sakatariyar jam’iyyar APC da ke Birnin Kebbi, lamarin da ya janyo artabu tsakanin magoya bayan Malami da ‘ya’yan jam’iyyar APC a jihar.

 
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara