Kungiyar likitoci masu neman kwarewa a Najeriya ta bayyana janye yajin aikin gargadi da ta tsunduma kwanaki biyu da farawa.
Kungiyar ta kuma bai wa gwamnatin tarayyar kasar wa’adin makonni biyu don biya mata bukatunta.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa tun a ranar Juma’a 12 ga watan Satumba kungiyar ta fara yajin aikin, kamar yadda shugaban kungiyar Dr. Tope Osundara ya bayyana a cikin wani sako.
A cewar sa, gwamnati ta biya wasu daga cikin bukatun da kungiyar ke nema, tare da alkawarta cika sauran, wadanda suka hada da tarin basuka, gyara musu tsarin albashi da dai sauran su.



