DCL Hausa Radio
Kaitsaye

KEDCO na barazanar katse wutar Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano kan bashi na Naira miliyan 949.88

-

Kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano KEDCO ya bukaci Asibitin koyarwa na Aminu Kano AKTH ya biya bashin wutar da ya sha wacce ta kai Naira miliyan 949.88 a watan Augusta, tare da kudin watan nan na Satumba 108.95m cikin kwanaki goma ko a katse musu wuta.

A cewar mai magana da yawun kamfanin, Sani Bala, asibitin ya kasa biyan kudin wutar da ake amfani da ita a gidajen ma’aikata, lamarin da ke shafar ingancin ayyukan KEDCO.

Google search engine

Jaridar Punch ta rawaito cewa KEDCO ya tabbatar da cewa manyan cibiyoyin lafiya a asibitin suna samun wuta daga 33KVA da ke ba da kimanin sa’o’i 22 na wuta a kowace rana.

Sai dai kamfanin na KEDCO ya ce kin amincewar AKTH a raba layukan wutar lantarki ta barngaren asibitin da gidajen ma’aikata ne ya jawo matsalolin katsewar wuta a kwanakin baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Bai kamata NAHCON ta fara shirin hajjin 2026 ba tare da ta bayar da bayanin kudaden da aka kashe a hajjin 2025 ba‘

Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Jin Dadin Alhazai ta Jihohin Nijeriya ta bukaci hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya (NAHCON) da ta gaggauta kammala daidaita bayanan...

Farfesoshin Nijeriya na cikin jerin na nahiyar Afrika da ba su da albashi mai kyau

Bayanan da jaridar Punch ta tattaro sun ce malamin jami'a a Nijeriya da ya kai matakin farfesa na samun matsakaicin albashi na dala 366 (kimanin...

Mafi Shahara