DCL Hausa Radio
Kaitsaye

KEDCO na barazanar katse wutar Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano kan bashi na Naira miliyan 949.88

-

Kamfanin rarraba wutar lantarki na Kano KEDCO ya bukaci Asibitin koyarwa na Aminu Kano AKTH ya biya bashin wutar da ya sha wacce ta kai Naira miliyan 949.88 a watan Augusta, tare da kudin watan nan na Satumba 108.95m cikin kwanaki goma ko a katse musu wuta.

A cewar mai magana da yawun kamfanin, Sani Bala, asibitin ya kasa biyan kudin wutar da ake amfani da ita a gidajen ma’aikata, lamarin da ke shafar ingancin ayyukan KEDCO.

Google search engine

Jaridar Punch ta rawaito cewa KEDCO ya tabbatar da cewa manyan cibiyoyin lafiya a asibitin suna samun wuta daga 33KVA da ke ba da kimanin sa’o’i 22 na wuta a kowace rana.

Sai dai kamfanin na KEDCO ya ce kin amincewar AKTH a raba layukan wutar lantarki ta barngaren asibitin da gidajen ma’aikata ne ya jawo matsalolin katsewar wuta a kwanakin baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara