DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi awon gaba da masallata da dama a jihar Zamfara

-

Akalla mutane 40 ne ake zargin ’yan bindiga sun sace da Asuba a wani masallaci da ke kauyen Gidan Turbe, ƙaramar hukumar Tsafe, jihar Zamfara.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:30 na asubar ranar Litinin yayin da suke tsaka da sallah.

Google search engine

Wannan harin ya nuna rushewar yarjejeniyar sulhu da aka kulla a watan da ya gabata tsakanin shugabannin al’umma da wasu daga cikin ’yan bindiga a Katsina da Zamfara.

Yarjejeniyar dai ta yi alƙawarin kawo ƙarshen hare-hare da garkuwa da mutane, tare da ba manoma damar yin noma a gonakinsu cikin kwanciyar hankali.

Sai dai kwatsam, wasu daga cikin ’yan bindigar sun ci gaba da kai hare-hare a jihohin arewa maso yamma.

Daily Trust ta rawaito cewa rahotanni sun tabbatar da dakarun Operation fansar yamma na ci gaba da sintiri da kai samame a yankunan da abin ya shafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Bai kamata NAHCON ta fara shirin hajjin 2026 ba tare da ta bayar da bayanin kudaden da aka kashe a hajjin 2025 ba‘

Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Jin Dadin Alhazai ta Jihohin Nijeriya ta bukaci hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya (NAHCON) da ta gaggauta kammala daidaita bayanan...

Farfesoshin Nijeriya na cikin jerin na nahiyar Afrika da ba su da albashi mai kyau

Bayanan da jaridar Punch ta tattaro sun ce malamin jami'a a Nijeriya da ya kai matakin farfesa na samun matsakaicin albashi na dala 366 (kimanin...

Mafi Shahara