DCL Hausa Radio
Kaitsaye

’Yan sanda sun kama mutanen da ake zargi da satar kifi a jihar Neja

-

Rundunar ’yan sandan jihar Neja ta sanar da kama mutane hudu bisa zargin sata da kuma karɓar kayan sata, bayan da aka sace kifaye da kimar kudinsu ta kai Naira 750,000 daga wani gidan gona a Lapai-Gwari, karamar hukumar Chanchanga.

Mai magana da yawun rundunar, SP Wasiu Abiodun, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa a ranar 8 ga Satumba, 2025, wasu mutane biyu, Hussaini Garba da Umar Danfulani, dukkansu daga Lapai-Gwari sun hada baki, tare da sace kifin a lokuta daban-daban.

Google search engine

Ya ce daga bisani an kama Garba, kuma yayin bincike ya amsa laifin, inda ya bayyana sunayen mutanen da ya ba su kifin da aka sace.

Rundunar ’yan sandan ta tabbatar da cewa ana ci gaba da bincike tare da farautar sauran masu laifi, tare da ba da tabbacin cewa za a gurfanar da duk wanda aka kama da aikata irin wadannan laifuka domin kare al’umma a Jihar kamar yadda Jaridar Punch ta Ambato.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara