DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mun kawo karshen dogayen layukan mai na shekaru 50 a Najeriya – Dangote

-

Mamallakin matatar mai ta Dangote, Aliko Dangote ya bayyana cewa shekaru akalla 50 da aka shafe a Najeriya ana fama da dogayen layuka a gidajen mai ya kawo karshe, tun bayan da matatar sa ta fara aikin tace fetur a shekarar da ta gabata.

 

Google search engine

Dangote ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a taron cika shekara guda da fara aikin matatar, inda ya ce tun daga shekarar 1975 ‘yan Najeriya ke fama da dogayen layukan.

 

Sai dai yace daga ranar 15 ga watan Satumban 2024 wannan matsala ta kau, biyo bayan fara aiki gadan-gadan, kamar yadda Channels TV ya wallafa.

 

Kazalika ya jaddada kudirin matatar man Dangote na ganin ta ciyar da Najeriya da ma nahiyar Afirka gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara