Kungiyar kasashen kawance na AES da suka hadar da Nijar, Mali da Burkina Faso wadanda sojoji ke mulki na bikin cika shekaru biyu da kafuwa.
A ranar 16 ga watan Satumban 2023 kasashen uku da sojoji suka yi juyin mulki suka sanar da kafa kungiyar, da zummar hada kai wajen yakar ayyukan ta’addanci da ke addabar su.
Wannan ya zo ne bayan da kasashen na yankin Sahel suka ayyana ficewa daga cikin ƙungiyar kasashen yammacin Afirka ECOWAS kan wasu zarge-zarge.



