Kungiyar dattawan Arewa ACF, ta mayar da martani kan kiran da gwamnan jihar Neja, Umaru Bago, ya yi na cewa ’yan siyasar Arewa su bari sai bayan shekara ta 2031 kafin su nemi shugabancin ƙasar.
A cewar Gwamna Bago, ya kamata a bar Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda ya fito daga Kudu, ya kammala wa’adin mulkinsa na shekara takwas kafin wani daga Arewa ya fito takarar shugaban ƙasa.
Sai dai sakataren yaɗa labaran kungiyar na kasa, Tukur Muhammad-Baba, ya bayyana cewa wannan magana ta Bago ba ta da wata madogara a kundin tsarin mulkin Najeriya.
Inda ya ce kundin tsarin mulki ya baiwa kowanne ɗan ƙasa damar tsayawa takara ko a zaɓe shi, babu wani tanadi da ya ce sai a dagawa wani kafa a neman takara.



