DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kasar Saudiyya ta saki wata ‘yar Nijeriya da aka tsare bisa zargin sanya miyagun kwayoyi a jakarta

-

Hukumomi a Saudiyya sun saki Maryam Abdullahi Hussaini, ‘yar asalin Nijeriya daga jihar Kano, wadda aka tsare a Makkah bisa zargin ta da jaka mai dauke da miyagun kwayoyi.

Kazalika, an kuma saki wasu ‘yan Nijeriya biyu Abdullahi Bahijja Aminu da Abdulhamid Saddiq da su ma suka fuskanci irin wannan tuhuma.

Google search engine

 

Maryam, ta samu ‘yancin ne bayan kwashe sama da mako biyar a tsare, sakamakon shiga tsakani da gwamnatin Nijeriya da kuma tabbatarwar da hukumar NDLEA ta yi cewa ba ta da laifi.

Jaridar Premium times ta rawaito cewa mijin matar Abdullahi Baffa, ya tabbatar da sakin nata, inda ya bayyana farin cikinsa tare da gode wa Allah da dukkan masu hannu a lamarin.

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya NDLEA ta bayyana cewa binciken da ta gudanar ya gano cewa matasa masu safarar miyagun ƙwayoyi a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano ne ke shirya makirci, ta hanyar saka sunayensu jakunkuna da ba na fasinjojin ba.

An kuma tabbatar da cafke shugabansu Mohammed Ali Abubakar, da wasu daga cikin mabiyansa, wadanda ke da hannu wajen sakawa fasinjojin da ba su da laifi cikin wannan tarkon.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara