DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wike ya ce zai kyale Fubara ya yi gaban kansa a zaben kwamashinoninsa

-

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya bayyana cewa ba shi da wani shiri na ba wa gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, shawarar sunayen kwamishinoni a sabuwar gwamnatin sa.

Wike ya bayyana hakan ne a shirin Politics Today da gidan talabijin na Channels ranar Alhamis, bayan dawo da gwamnatin Fubara daga dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Tinubu ya ayyana a jihar tsawon watanni shida.

Google search engine

A watan Maris ne aka ayyana dokar ta-ɓacin, bayan rikicin siyasa tsakanin Fubara da Wike ya kazanta, wanda da dama suka danganta shi da zargin cewa Wike yana tursasa wa Fubara nada mukarraban sa a gwamnati.

Sai dai Wike ya ce yanzu bai da wanda zai ba da shawarar sunansa, yana mai jaddada cewa zai bar wa gwamnan cikakken ikon gudanar da harkokin mulkin jihar mai arzikin mai a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara