DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wike ya amince da bukatun likitocin Abuja da ke yajin aiki

-

Ministan babban birnin tarayya Nyesom Wike, ya amince da dukkan bukatun likitoci masu neman kwarewa da suka shiga yajin aiki tun ranar 15 ga Satumba, saboda batun albashi da alawus-alawus din su.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Juma’a yayin kaddamar da aikin gina hanyar Northern Parkway daga Ring Road II zuwa Ring III a kan titin Shehu Yar’Adua, a birnin Abuja.

Google search engine

Haka kuma, ya umurci mukaddashin Shugaban ma’aikatan FCT tare da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin gudanarwa, Samuel Atang, da su aiwatar da umarnin yadda ya kamata.

Rahoton kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN, ya tuna cewa likitocin sun shiga yajin aiki bayan doguwar tattaunawa da hukumar FCTA ba tare da samun mafita ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara