DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba za a dawo daukar fasinjojin Kaduna-Abuja ba har sai mun tabbatar da komi ya koma dai-dai – Hukumar kula da jiragen kasa ta Nijeriya

-

Hukumar kula da jiragen kasa ta Njeriya NRC ta bukaci ma’aikatanta da ke aiki a layin jirgin kasa na Abuja zuwa Kaduna da su bi doka da ƙa’idojin aiki cikin tsanaki, musamman bayan hadarin da ya faru da jirgin a ranar 26 ga Agusta, 2025.

Babban Daraktan hukumar Dr. Kayode Opeifa ne, ya bayyana haka ne a Lagos a ranar Juma’a, yayin da yake gabatar da sakamakon binciken da aka gudanar kan hatsarin.

Google search engine

Ya ce kafin a dawo da jigilar fasinjoji, dukkan ma’aikatan za samu horo na musamman na kwanaki hudu daga ranar Litinin, 22 ga Satumba, domin tabbatar da tsaro da ingancin aikinsu.

A cewarsa ba za a fara jigilar fasinjoji ba har sai an tabbatar da komai ya koma daidai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara