DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Neman zaman lafiya ya hana ni kalubalantar dokar ta baci a Ribas – Fubara

-

Gwamnan Ribas Siminalayi Fubara ya bayyana cewa neman zaman lafiya, daidaito da kuma ci-gaba ne ya sanya shi kin kalubalantar dokar ta bacin da shugaba Tinubu ya ayyana a jihar.

Gwamnan ya yi wannan furuci ne a jawabinsa ga ‘yan jihar a ranar Juma’a, biyo bayan karewar wa’adin dokar da shugaban ya ayyana, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.

Google search engine

A cewar Fubara, ya fuskanci matsi daga magoya bayansa domin ya kalubalanci dokar, sai dai ya ki amincewa da hakan.

Kwanaki biyu bayan janye dokar ne gwamnan da mataimakiyarsa tare da shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin jihar ta Ribas suka sauka a filin sauka da tashin jirage na Fatakwal.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara